13/08/2026
TIRƘASHI: "Kafin Zuwan Tinubu Kowace Rana Sai An Kashe Mutum 9 An Sace Mutane 15 A Jihar Katsina Amma Bayan Zuwan Tinubu Sai Da Aka Yi Wata 8 Ba A Sace Ko Mutum Ɗaya Ba", In Ji Darma
A cewar ministan gidaje, Injiniya Muttaƙa Rabe Darma, an samu gagarumin ci gaba sosai kan harkokin tsaro a gwamnatin Tinubu duba da yadda matsalolin kashe-kashe da garkuwa da mutane s**a kau, musamman a Jihar Katsina.
Dokin Ƙarfe TV ta jiyo Darma na bayyana hakan a tattaunawarsa ta kai tsaye da DCL, inda ya tabbatar da cewa hatta garuruwan da ada ba sa iya noma da fita sallar Asuba saboda matsalar tsaro yanzu komai ya daidaita duk da cewa matsalar ba wai ta kau gaba ɗaya ba ne.
Darma ya kuma jaddada aniyarsa ta ci gaba da tallata gwamnatin Tinubu a Arewa, domin a cewarsa rashin maganar ire-irensa masu muƙamai ita ta buɗe ƙofar da har ƴan adawa ke baƙanta musu gwamnati alhalin kuwa Tinubu shugaba ne na gari mai sauraron koken jama'a.
"Bayan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Ƴar'adu'a, ba a taɓa shugaban ƙasa mai sauraro da darajanta mutane kamar Tinubu ba. Komai yawan maganar da ka zo masa da ita zai tsaya ya saurare ka, kuma har ka ja ya ja saboda nagarta irin tasa. Amma akwai shugban da in ka ja da shi gobe ba zai saurare ka ba". In ji Darma.