23/07/2023
Hijirar Manzon Allah (SAWW) Daga Makka Zuwa Madina
Hijira Asalin kalmar Larabci ce da aka arota zuwa yaran Hausa, (ma'anar kalmar shine kaura daga wani guri zuwa wani guri, amman galibi domin samun Zaman Lafiya) wanda kalmar zata dace da ita a hausa itace Kaura, amman ma'anan kalmar a addinin Musulunci na nufin:- "Hijiran da Manzon Allah yayi ta re da Abubakar Siddiq (RA) daga Makkah zuwa Madinah (Yasrib) a shekarar 622) bayan kafi*ran makkah sun tsara su kashe shi a watan Janairun shekarar 622 Miladiyya sai Allah ya umurci Annabi (SAWW) da yayi Hijira daga Makkah zuwa Madinah, wanda a wancan lokacin a na kiran garin da Yasriba, zuwan Annabi garin keda da wuya, sai aka samawa garin suna da Madina ma'ana Birni.
Saboda ganin irin tasirin da Musulunci ke samu da kuma gazawarsu wajen dakushe haskensa, kafi*ran Makka sun shirya makirci na kokarin kashe Manzon ALlah (SAWW). Bugu da kari kuma rasuwar Abu Talib, garkuwan addinin musulunci ya dauke wani babban abin da ke kare su daga kashe Manzon (SAWW). To sai dai kuma ka*firan Makkan su ka shiga kulle-kullensu ba tare da la'akari da cewa Ubangiji Allah Ya na sane da abin da suke kullawa ba.
Bayan sun gama yanke shawarar kashe Manzon Allah (SAW), sai Allah (SWT) Ya sanar da shi labarin abin da suke kullawa, sannan Ya ba shi umarnin ya yi hijira ya bar Makka zuwa garin Madina. Allah (SWT) Ya na fadi a cikin Alkurβani Mai girma cewa:
βKuma a lokacin da wadanda s**a kafir*ta suke yin makirci game da kai, domin su (daure ka), ko su kashe ka, ko kuma su fitar da kai (su kore ka daga Makka), su na makirci kuma Allah Ya na mayar musu da makirci, kuma Allah ne mafificin masu makirci.β (Anfal:30).
Wannan umarni dai na Ubangiji ya biyo bayan taron da Kuraishawa s**a yi a wajen taronsu na Darul-Nudwah, in da su ka yanke shawara a kan kashe Annabi (SAWW) ta hannun wasu gungun 'yan iskan gari da ya kunshi mutum daya ko biyu daga kowace babbar kabila daga kabilun Kuraishawa, don jinin shi ya tafi a banza; wato ya bace a tsakanin kab