14/06/2026
Muhsin Imam
---
*Assalamu Alaikum Jama'ar Kauru Mai Daraja,*
Ni ne ɗan'uwan ku *Muhsin Imam*.
Na buɗe wannan shafi na "Mai nasara GIDA GIDA" ne domin mu yi magana kai tsaye, gida-gida. Burina ɗaya ne: *In ga al'umma talakawa sun ci gaba a Kauru da Nigeria baki ɗaya.*
A matsayina na dan takara a karkashin jam'iyyar *ADC*, na zo da alkawari, ba da siyasar yaudara ba. Zamu mayar da hankali kan:
1. *Magance matsalar ruwan sha* a dukkan kauyukan Kauru
2. *Bunkasa noma da sana'o'in hannu* ga matasan mu
3. *Inganta makarantunmu da asibitoci*
Wannan tafiya ba tawa ba ce - *tamuyar mu ce, mu 'yan Kauru*. Kujerar nan tamu ce baki ɗaya.
*Ina roƙon ku:*
1. *Ku bi shafin nan* 👆 don mu kasance tare kullum
2. *Ku raba wannan saƙon* da dukkanin 'yan uwa da abokan arziki a Kauru
3. *Ku rubuta a comment*: Wace matsala ce ta fi damun ku a Kauru yanzu? Ina son ji daga bakin ku.
Allah ya ba mu nasara. Gida-gida zamu kai saƙon cigaban Kauru!
*Muhsin Imam*
Dan Takara, ADC - Kauru
*