16/05/2026
YAU 16/5/2026 DA MISALIN 2:00 PM
WATA ZAI SHIGA CIKIN MANZILAR HAQ’AH
A Burjin Sauru, a mataki na 21
A ilimin manazilul qamar, Haq’ah yana daga cikin masaukai masu rikitarwa. Masauki ne da yake ɗauke da haɗuwar alheri da rashin alheri a lokaci guda, saboda yana tsakanin ƙarfin Sauru da Jauza’a.
Masanan taurari sun yi gargadi game da fara manyan ayyuka masu muhimmanci a irin wannan lokaci, musamman: ƙirƙira, gina sabuwar hanya, shuka, girbi, ƙulla yarjejeniya, ko fara abin da mutum yake son ya daɗe yana amfanar sa.
Ana ganin cewa abubuwa da yawa da aka fara a irin wannan lokaci s**an fuskanci: jinkiri, lalacewa, rikicewa, ko rashin cikar buri yadda ake fata.
Sai dai duk da haka, wannan masauki yana da alaƙa da: magance wasu gubobi, haɗa magunguna masu ƙarfi, da bincike kan cututtuka masu tsanani.
Wato masauki ne da yake iya zama waraka ga wani abu, amma kuma ya zama lalacewar wani abu idan ba a yi hattara ba.
A wasu tsofaffin littattafan taurari an ambaci cewa: “Ba kowane lokaci ne ya dace da fara al’amari ba. Wasu lokuta hikima ita ce jira.”
Saboda haka masu ilimin taurari kan fi bada shawarar: idan ba dole ba ne, a dakata da manyan tsare-tsare har sai Wata ya wuce wannan masauki.
Idan kuma wani abu ya zama dole a aikata, ana son: sadaka, yin addu’a, da neman kariya kafin fara aikin.
Abin mamaki kuwa shi ne: akwai lokutan da mutum zai yi duk ƙoƙari, amma lokaci shi ne yake hana abu tabbata.
Allah ne mafi sani.
+22788814017
asheik Muhammadul aminu alkadiree