02/05/2026
DA DUMI-DUMI: Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi su na shirin ficewa daga jam’iyyar ADC
Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, tare da tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, su na shirin ficewa daga jam’iyyar ADC, kamar yadda rahotanni s**a bayyana.
Majiyoyi sun bayyana cewa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ne yake kokarin hada kawance a tsakaninsu domin samar da sabuwar hadakar siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2027.
Yayin da aka hangi wasu makusantan siyasar Kwankwasiyya sun fara ficewa daga jam'iyyar ADC a safiyar yau.
Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin tunkarar zaben 2027, inda manyan ‘yan siyasa ke sake tsara matsayinsu domin samun karfi a fagen siyasa.
Shin kuna gani wannan hadaka za ta iya tasiri a zaben 2027?