مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا

  • Home
  • Nigeria
  • Danja
  • مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا

مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا The First Islamiyya School in Ɗanja Local Govt

SAKON GODIYA DA BANGAJIYAAssalamu Alaikum A madadin shugaban wannan Makaranta Madarasatu zikra Shehu Usman Bin Fodiy Dan...
09/02/2026

SAKON GODIYA DA BANGAJIYA

Assalamu Alaikum

A madadin shugaban wannan Makaranta Madarasatu zikra Shehu Usman Bin Fodiy Danja, Imam Suleiman Sani Danja (Babban Limamin Jumuah na Garin Danja) Muna miƙa sakon godiya tare da bangajiya ta musamman ga dubban al’ummar da s**a halarci gagarumin taron Walimar Saukar Alkur'ani Mai girma na Dalibai guda 102.

Hakika halartar ku da goyon bayan da kuka nuna ya ƙarawa wannan taro armashi da nasara.

Muna miƙa godiya ta musamman ga manyan baƙi da s**a tallafa, s**a ba da gudunmawa, kuma s**a tsaya tsayin daka wajen ganin wannan taro ya gudana Cikin Nasara.

Cikin girmamawa da mutuntawa muna mika godiya ga:
1. Hon. Abdullahi Balarabe Dabai – Memba a Majalisar Wakilai ta Tarayya (Bakori/Danja Constituency).
2. Alh. Sani Sabiu – M.D/C.E.O, AS&S Alheri Bread Danja.
3. Alh. Aminu Lawal – Shugaban Katsina State Traders Union, reshen Karamar Hukumar Danja.
4. Alh. Adda’u – C.E.O, Rahamaniyya Bread.
5. Alh. Yazid Abubakar – Sarkin Fulanin Danja kuma wakilin Hakimin Gundumar Danja.
6. Alh. Sani Sunusi – Shugaban Kasuwar Tumatur ta Danja.
7. Alh. Mahmud Nuhu - M.D/C.E.O M,Lovers Special Bread
’Yan Kasuwar Filin Tumatur, da kuma sauran ’yan kasuwa na fadin Karamar Hukumar Danja.

Haka nan, muna mika godiya ga Malamai, Iyaye, Masu ruwa da tsaki, da dukkan al’ummar da s**a Sami halarta da kuma waɗanda ba su samu damar halarta ba amma s**a ba da gudunmawa ta hanyoyi daban-daban ta kuɗi, addu’a, shawara ko ƙarfafa gwiwa. Lallai gudunmawar ku ta taka muhimmiyar rawa wajen nasarar wannan gagarumin taro.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saka muku da alheri, Ya ninka ladan duk abin da kuka bayar, Ya albarkaci rayuwarku da dukiyarku, kuma Ya biya ku da Gidan Aljannah.

Mungode ƙwarai da gaske. Allah Ya saka da alheri.

Alhamdulillah Kamar kowacce Shekara yauma Ɗaliban مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا Karkashin Zawiyyar Imam Sulaiman S...
24/12/2025

Alhamdulillah
Kamar kowacce Shekara yauma Ɗaliban مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا Karkashin Zawiyyar Imam Sulaiman Sani Mai Islamiyya (Chief Imam Danja) mun gudanar da Mauludin Fiyayyen Halitta Annabi Sallallahu Alaihi wa sallam, muna mika godiya ga Allah Subhanahu wa Ta'ala da ya bamu iKon gabatar da wannan munasaba na Mauludi lafiya Kuma muka kammala lafiya, sannan muna mika godiya da bangajiya ga bakinmu musamman 'yan Islamiyyu na fadin Karamar Hukumar Danja wadanda s**a Sami damar halarta da wadanda basu Sami damar halarta ba Allah Ya sakawa kowa da Alkhairi Ya maimaita mana.

mun gode

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِإِنَّا لِلَّهِ وَإِنَّا إِلَيْهِ رَاجِعُونَبمزيد من الحزن والأسى نتقدّم بخالص التعا...
10/09/2025

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ
إِنَّا لِلَّهِ وَإِنَّا إِلَيْهِ رَاجِعُونَ

بمزيد من الحزن والأسى نتقدّم بخالص التعازي والمواساة إلى الإخوة والأهل وأهالي مدينة بَكُوري في وفاة الإمام الكبير، إمام الجمعة لمدينة بَكُوري الشيخ سعد ثاني بَكُوري.

نسأل الله العلي العظيم أن يغفر له، ويرحمه رحمة واسعة، ويتقبّل أعماله الصالحة، ويعفو عن خطاياه، وأن يبارك في ذريته، ويجعلهم من الصالحين. آمين.

24/08/2025

وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ فِيكُمۡ رَسُولَ ٱللَّهِۚ
Barka da Zuwan Watan Haihuwar Manzon Tsira Sallallahu Alaihi wa sallam

Assalamualaikum Muna gayyatar Kowa Maulud Gobe Idan Allah Ya kaimu
24/12/2024

Assalamualaikum Muna gayyatar Kowa Maulud Gobe Idan Allah Ya kaimu

Address

Danja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when مدرسة ذكرى الشيخ عثمان بن فودي طنجا posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share