25/03/2026
MAKARANTAR MARKAZUL IHSAN
Sanarwa ta Musamman
Rana: 25 ga Maris, 2026
Iyaye/ Masu Kulawa,
SANARWAR DAWOWA MAKARANTA BAYAN HUTUN RAMADAN
Muna gode wa Allah Madaukakin Sarki da Ya ba mu ikon kammala azumin watan Ramadan lafiya.
Ana sanar da ku cewa za a koma makaranta domin ci gaba da karatu bayan hutun Sallah a ranar Asabar, 28 ga Maris, 2026. Ana sa ran dukkan dalibai za su dawo a kan lokaci kuma cikin shiri.
Haka kuma, ana sanar da ku cewa za a fara jarabawar CA (Continuous Assessment) nan ba da jimawa ba bayan dawowa. Saboda haka, a tabbatar dalibai sun shirya sosai.
Bugu da ƙari, muna tunatar da iyaye/masu kulawa cewa biyan kudin makaranta wajibi ne. Duk dalibin da bai cika biyan kudin makaranta ba, ba za a ba shi damar ci gaba da zama a makaranta ba.
A tura kudin makaranta ta wannan asusun:
Sunan Asusu: Metro School
Banki: Stanbic IBTC
Lambar Asusu: 0010048266
Muna gode da hadin kan ku da goyon bayan ku.
Na gode.
Hukumar Gudanarwa
Makarantar Markazul Ihsan